Wasu matasa a garin Magazu da ke karamar hukumar Tsafe a jihar Zamfara sun afkawa ofishin ‘yan sandan yankin inda suka kona shi kurmus sakamakon rashin jitawar da ya shiga tsakanin matasan garin da ‘yan sandan.
Matasan sun zargi ‘yan sandan da yin sanadiyyar mutuwar wani matashi mai suna Ibrahim Muhammad a hannun ‘yan sandan bayan garkame shi da suka yi a ofishinsu.
Wani ganau da ya so asakaya sunansa ya bayyanawa LEADERSHIP HAUSA cewa, mutumin da ya rasu ‘yan sandan zarginsa ne da sace wayar sadarwa.
Kakakin hukumar ‘yan sandan jihar Zamfara Shehu Muhammad ya tabbatar da aukuwar lamarin kuma ya ce, hukumar za ta tsaurara bincike.
Daga Leadership Hausa
Tags:
LABARI